Yan arewacin Najeriya da ke zaune a kudu maso gabashin kasar sun ce sun tafka asarar rayuka da ta dukiya sakamakon rikicin da masu fafutikar kafa kasar Biafra suke yi a yankin.
Sun shaida wa wakilinmu na yankin Abdussalam Ibrahim Ahmed cewa an kashe mutanensu da dama da kuma kona dukiyarsu.
Sai dai jami'an tsaro sun ce ba a samu asarar rayuka ba kawo yanzu.
Source: BBC Hausa