Shugaban Majalisar Wakilan Najeriya Yakubu Dogara ya ce Shugaban Kasar Muhammadu Buhari ya murmure bayan ya kwashe fiye da wata uku yana jinya a birnin Landan.
Dogara ya bayyana hakan ne bayan ya ziyarci shugaban a gidan yake jinya a birnin Landan ranar Alhamis.
Ya ziyarci shugaban ne tare da Shugaban Majalisar Dattawa Bukola Saraki.
Source: BBC Hausa