Hukumar EFCC Ta Garkame Tsohon Gwamnan Jigawa, Samunu Turaki Bisa Zargin Wawushe Dukiyar Jiharsa A Lokacin Da Yake Gwamna
Hukumar EFCC ta tsare tsohon gwamnan jihar Jigawa Ibrahim Saminu Turaki a ofishinta dake Abuja.
Ana zargin Saminu Turaki da wawushe kudaden jihar Jigawa a lokacin da yake gwamnan jihar Jigawa.
Hukumar ta ce ba za ta saki Saminu ba har sai ranar da za ayi zama na gaba a kotu domin ci gaba da sauraren karan.