Jami’an ‘Yan Sanda sun gano wani gidan makamai a Yankin Tse-Tyungu dake Jihar Benuwe inda har aka kama mutane 3 da ake zargi da hannu wajen harkar. Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Bashir Makama ne ya tabbatar da hakan.
Kwamishinan ya ce dubun masu mummunan laifin ya cika a daren jiya.
Da alamu dai an saba kera mugayen makamai a gidan daga nan kuma ake saidawa a sauran wurare. Cikin kayan da aka samu har da tukunyar gas da babur da zarto.