A watan Nuwamba ne dai wasu suka kama Ambasada Bagudu Hirse Mammam tsohon minista, a daidai kofar gidan Mammam Daura dake Kaduna.
Rahotanni sun nuna cewa jami'an tsaro sun kamo su, tare da muggan makaman da suke amfani dasu wajen aikata mummunan aikin satar mutane.