Shugaban Rundunar 'Yan sanda ta Kasa, Ibrahim Idris ya bayyana dalilin da ya sa 'yan sanda suka bude wuta kan mabiya Shi'a a Kano inda ya nuna cewa 'yan Shi'an na dauke da makamai a lokacin arangamar.
Ya ci gaba da cewa rundunar ba za ta kyale wasu tsiraru da ke neman kawo rudani a cikin kasa ba ba ya ga kashe jami'an tsaro da sunan neman 'yancinsu inda ya kara da cewa nauyin rundunar ce na kare dukiyoyi da rayukan 'yan Nijeriya.