Gwamnatin jihar Kaduna ta sanar da cewa lallai za ta fara aikin gina sababbin titunan jirgin kasa a fadin jihar daga shekara mai zuwa.
Gwamnatin tace da ga farko za a dauko titin da ga garin Rigachikun Zuwa Matatar mai na kasa dake gaba da Sabon Tasha, Kaduna.
Gwamnati tace za ta kasafta naira Biliyan 4 domin fara hakan.
Bayan haka kuma gwamnatin ta ce za ta siyo jirage masu tuka kansu da kuma na'uran kallo mutane domin samar da tsaro a jihar.
Premium Times Hausa