Shi dai wannan matashi mai suna Mustapha Usman Hassan (Yekini) wanda haifaffen unguwar Bolari ne dake jihar Gombe, yana aiki ne da wata ma'aikata a babban birnin tarayya a Abuja.
Wani abin burgewa ga wannan gudummawa da matashin ga bayar, shine ya yi hakan a kashin kansa ba wai a gwamnatance ba. Kuma akwai bukatar masu dama irin tasa da su yi koyi da shi domin tallafawa marasa karfin da suke yankunansu.