Kamar yadda wani mai suna Zannah ya sanya a shafinsa na Facebook, tsohuwar mai suna Hajja Gotowa Abdullahi daga gundumar Bulabulin dake garin Maiduguri, ta bayyana cewa duk wani mai adawa da gwamnatin Muhammadu Buhari dan Boko Haram ne.
Tsohuwar dai ta bayyana hakan ne biyo bayan irin nasarorin da shugaba Buhari da sojoji suka samu wajen yakar Boko Haram a yankin Arewa maso Gabas.