Sakamakon jita-jitar da ake ta yadawa na cewa an jefi gwamnan jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje a masallacin Juma'a yau, rahotanni daga fadar gwamnatin jihar ta Kano, ta bayyana cewa yanzu haka gwamnan yana kasar Saudiyya domin gudanar da aikin hajji.
A makon da ya gabata ma dai, wasu kafafun yada labarai sun yada labarin cewa an jefi gwamnan a masallacin, alhalin kuma a masallacin gidan gwamnati ya yi sallah.