Sojojin Nijeriya Sun Kashe 'Yan Boko Haram Guda Goma Tare Da Kama Biyu A Raye, A Yayin Wata Farauta Da Suka Fita A Garin Chukungudu Da Hausari A Jihar Borno A Jiya Juma'a.Haka kuma sojojin sun ceto wata mata da yarinyarta wanda 'yan Boko Haram din suka sace. Sannan kuma an kwace makamansu da dama.