Dakarun sojojin Nijeriya a jiya Litinin sun yi nasarar ceto wasu mutane kimanin dari biyar, wadanda akasarinsu mata ne da yara, a yayin wata farauta da suka fita a yankunan Mafa, Dikwa da Kala dukkansu a jihar Borno.
Bincike ya nuna cewa yankunan na fama da hare-haren 'yan Boko Haram.
Haka kuma sojojin sun yi nasarar kashe 'yan Boko Haram guda hamsin tare kuma da kwace makamansu.
*Nan wasu daga cikin hotunan 'yan bindigan da aka kashe ne da kuma wadanda aka ceto.