Hukumar EFCC ta soma gudanar da bincike kan gwamnatin tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shema.
Majiyarmu ta Daily Trust ta rawaito cewa har zuwa lokacin da ake kan hada wannan rahoto, jami'an hukumar suna kan ganawa da wasu daga cikin tsoffin mukarraban tsohon gwamnan da ma na yanzu.