Hausawa suka ce "Zo mu zauna, zo mu saba" in dai har mutum biyu za su yi alaqa kowace iri ce kuwa dole a sami dalilin da zai hada su rikici, sai dai ana sa rai za su sami abin da zai janyo hankalinsu su daidaita tsakaninsu, galibin abubuwan da suke hada mutane fada su ne:-
1) Rashin damar fahimtar juna a tsakanin maneman guda biyu, shi saurayin ya gaza fahimtar cewa ita fa mace ce, kuma qasa da shekarunsa, ba ta alaqoqi da mabambantan jama'a kamar yadda yake da su, kuma takan dogara ne kawai da abin da zuciyarta ta ba ta, ita kuma ta kasa gane cewa shi maigidanta ne ba tsaranta ko qaninta ba.
.
2) Sai kuma rashin daidutuwar yanayi a tsakaninsu, wani namijin mai kishin gaske ne ga azaban riqo, ita kuma tana da samarin da ta saba da su tun kafin ta fara ganinsa, amma lokaci guda sai ya nemi ya raba ta da su, ko in yagan ta da wani namiji ko bai san me suke tattaunawa ba sai nan take ya haye, ko ta ba shi haquri sai ya yi kamar zaginsa ta yi, ita kuma ta ga cewa ba za ta yarda da wannan ba, ko kuwa ta ce ba ta riga ta zama matarsa ba don haka ba wata dokar da zai iya qagara ma ta, saurin fushi, ko zargi ba dalili, ko yawan surutu a kan masoyi yana saurin kawo matsalar rabuwa tsakanin manema.
.
3) Wani lokaci kuma akan sami sabani ne game da abin da ya shafi kudi, sau da yawa zumbuli bai qaunar abin da zai tabi aljuhunsa, in ya kasance yarinya mai yawan roqo ce, ko mai kwadayin abin hannun saurayi ce tabbas dayan abu biyu zai faru, ko dai ya yi sa'ar sauke ma ta inji, ko ya nemi rabuwa da ita, gwargwadon yadda mace ba ta qaunar marowaci da mai qoro, haka namiji ba ya son mace mai kwadayi da mai roqo, Annabi ya fadi a wani hadisi cewa: Ka guji abin hannun mutane sai su so ka.
.
4) Wani sa'in kuma ba wadannan kadai ba, in ya kasance daya cikinsu bai iya ma'amalla ba tabbas dayan zai guje shi, mace mai yawan feleqe da surutu, da harka da wasu mazan ba kamun kai, ko ba ta wani abu da su, samarin sukan guje ta, haka namijin da bai iya gyara kansa bai sakin fuska, sau da dama 'yammata sukan ji tsoronsa, in ka zama mai kwakwazo da yawan fada, lallai za ka kori 'yammatan da suke zagaye da kai.
.
5) Wani lokacin kuma tazarar da ake samu a tsakanin masoya ce take wargaza kan manema, na san wani mutum mai haiba da sifar girma, in ya dau wanka sai ka yi zaton wani alhaji ne, ya sami kansa cikin soyayya da wata lauya, alhali shi ko digiri bai fara ba, abokansa da dama ba su goyi baya ba, haka malamansa, ban san uwayensa a cikin gida ba, to ko shi ne ya ba ta tazara mai fadin gaske zai riqa raina ma ta a abubuwa da dama, ko ma ya riqa kiranta jahila, shi ya sa wasu lokutan akwai buqatar duba daidaituwar wayewa, masamman in ya kasance ita ce a gaba da shi.
.
6) Sabanin fahimta ta bangaren addini: Wannan ina nufin masu addini guda kamar 'yan Izala da 'yan dariqa, wadan da a fahimtar aqida suka sami sabani ba wai a ita kanta aqidar ba, koda yake an fara gyara wasu abubuwan a yau, dan Izala yana iya auren 'yar dariqa, a baya in uba ya ji cewa dan Izala ne saurayin 'yarsa sai dai su rabu, yanzu kuwa ba haka ba ne, amma tabbas Shi'a wani sabon addini ne wanda ya zama dole uwaye su san inda za su sanya diyarsu, sau da yawa mace tana kan fahimtar mijinta ne.
.
7) Shigar wasu bangarori cikin lamari tana daya daga cikin musabbaban haifar da sabani a tsakanin manema guda biyu, wasu qawayen ba su da adalci, dazarar wata qawa ta sami saurayi na gari sai ta yi qoqarin zugata ta yi masa laifin da za su rabu har abada, daga bisani kuma ita ta tura kanta, wani lokacin kuma abokai ne suke hana saurayi ya daidaita da yarinya, sau da yawa wata takan sami saurayi na qwarai, in wani ya taba nemanta ta wulaqanta shi, sai ya yi aiki da wasu wadan da za su kai gulmar cewa 'yar iska ce ko tun farko, na taba jin wace aka soka wai ta yi fim din batsa, nan take aka watsa tsakaninta da saurayin.
.
8) Uwaye mata ma ba a bar su a baya ba, in ya kasance uwar tana da wanda ta ajiye zai auri 'yarta, masamman in dan uwanta ne, to ko yarinya ta yi saurayi a waje da wahala in uwar ba ta raba tsakaninsu ba, haka in kishiyar uwar ce take riqon yarinyar, ya zamo uwar ba ta a gidan, kuma tana kishi da uwar, ga 'yar ta sami saurayin kirki, in ba a yi sa'a ba ita ma matsala ce, don kuwa za ta iya qulla makircin da za ta raba su, su kuwa maza wannan na kai tsaye ne, wani lokaci ko sabanin fahimta ce a tsakaninsu da uwayen yaro ko yarinya auren da ba za a yi ba kenan.
Title :
Bambanci Sha'awa Da Soyayya Part 11
Description : Hausawa suka ce "Zo mu zauna, zo mu saba" in dai har mutum biyu za su yi alaqa kowace iri ce kuwa dole a sami dalilin da zai hada...
Rating :
5