Bayan sun mini nasihohi aka kwasheni sai gidan mijina, su zainab khalifa da fatima duk an kawo jiki ana jiran ango da abokan ango Suxo ko za'ayi sa'a asamu wanda zai taya, amma har gurren 12:30 na dare ba ango ba abokanshi haka suka gaji da jira suka tafi gida, suna cixon yatsa" nima abdool xee khalifa ta bani tausayi danaga kwalliyar data chaba��
"
Annoucement.."yau rubutuna dayawa ta operane xakagani gaba daya"
Naziah dai haka ta zauna jugum sunaa fita ta kulle daki, dan ta cika alqawarin deen dinta,
Nayi bacci na, ga zafin da gabana yake min na wahalar da deen ya bani, cikin bacci nayi ta mafarkinsa...!!
Ji nayi an bubbuqa mini qofa, in fito ashe har 11 na safee yayi, na fito wai zamuje walimar da akeyi bayan amarya da ango sunyi Xxxxxxxx.. na buqa gafa ni wallahi banida lafiya!! akayi sama da qasa in xo muje naqi zuwa suka gaji suka kyaleni,
Bangaren nura kuwa yayanshi yayi rantsuwa idan har baije walimar nan ba sai yaci mutuncinsa, kuma bashi bashi har abada, dan ya zubar masa da mutunci iya zubarwa ranar daurin aure da baijeba, bama daurin aureba duk wani events da aka shirya nura bai halarci ko daya ba, haka dai ya shirya yaje walimar bada son ranshi ba wannan karon kuma ba amarya..
Walima tayi walima, an raba kayayyakin aure, gaskiya yayan nura mutumin kirkine kuma ya fitarda dan uwansa kunya, inaga walimar da akayi ba'ataba yin irinta ba duk sokoto, sabida komai need, anyi lafiya an qare lafiya an bar amarya da angonta da kuma halayensu......
Nura ya siyo wa matarshi sabuwar waya kuma aciki yayi saving din numbersa da sunanshi, koda bashida number ta amma ya mata letter yace duk duk abinda take buqata ta mishi sms a wayan da ya aiko ya ijiye mata akan hanyar dakinta..
Bangaren nura dana nazia daban ne, batasan shigarshiba batasan fitarshiba, haka shima,m baisan chinta ba baisan shantaba, kullum yana manne da waya yana waya da abar qaunarshi hulwaty azeez dinsa,.itama dai haka, suna farantawa juna rayuwa da kuma jaddada alqawuran da suka yiwa juna na kada ta kuskura mijinta ya kusanceta ita kuma tace kada ya kusanci matarshi.....
Haka rayuwar aure ta kasance, mata tun tana kulle qofarta har ta gane cewa mijin nan nata yafita qiyayyarta, sabida haka saim ta dan saki jiki ta rage zaman daki tana zama parlour tayi kallon ta tayi chatting dinta, a groups chat, dama mayyar chatting ce idan sun hadu da abdool a group din kar mu shagala ayita wasa da dariya kamar dama sun san juna su suke debe mata kewa, idan ana zolayarta da zancen banana takanyi murmushi aranta tace da deen dina bai dandana min ba ina har in koma ga mahaliccina indai akan wannan mijin nawane bazan san komai akan banana ba...
Gashi duk wani salon sarrafa namiji ta koyo shi sai dai ba mijin kuma bata buqatar sa a tunanin ta anyitane dan deen dinta....
wasa wasa naziah tayi wata biyu gidan nura, kullum cikin liSsafi take, yanxu ya rage saura wata biyu ta kashe aurenta taje gurin abin qaunarta tanata shirya plane na yanda xata bullo ma abin ya sallameta cikin mutunci dan ta kula shima dan is ne....
Bayan wata biyu ne yayan nura ya shirya mana tafiya honey moon a turkey, Cyprus da India, nidai kam sai sms ya mini wai inje kaduna gobe amini passport in shirya driver zai kaini, araina nace kuma uwar me xa'ayi da passport har baxan je ba kuma Sai na tuna da yaya yace ko banyi dan kowa ba nayi dan yayan shi...
munyi passport da komai, aka karbo mana visa da ticket da komai tafiya ta kankama na gama shirina koda ni ba son tafiyar nake yiba dan ina gudun achan ya sami sa'ata ya bata min shiri amma haka nayi biyayya ga karamcin da yayansa yake min yasa na amince..
Na fito parlour ina jira sai sms naji ya shigo "kije driver zai kaiki airport zanzo daga baya" araina nace tafi nono fari, na kira deen dina na gaya mishi zanyi tafiya yace shima zaiyi tafiya amma ya chanza bucking dinsa, naje airport driver ya bani dollars rapper daya nidai bansan ko nawa bane amma nasan suna da yawa, na saka jaka, har jirginmu ya kusa tashi baizo ba araina nace kardai ya wuce cikin jirgin b an ganshiba tunda ba saninsa nayiba, nayi hanxari na shiga jirgi, ko minti uku banyiba da zama ba sms ya shigo,
Bazan sami damar zuwa yauba, idan kin isa let me know..!! haushi ya kamani, ya zai turani wata qasa ni kadai, amma van damuba sabida nafi buqatar haka...
Na isa Cyprus lafiya, qasace ta arna ga tsadar rayuwa, dala 100 idan na fitar ko abincin kirki banaci in qoshi da ita, ni kadai nake holewata, na sayi sim C guda biyu daya a dayar wayata daya a tablet dina, na kira deen dina na fada mishi na iso lafiya, na kira iyayena na gaya musu na iso lafiya, layin da nake kiran deen daban wanda na kira gida daban, ban kira nura ba dan banida Lokacin sa, sati na daya a Cyprus deen dina ya baqunci qasar, tunda yazo muke tare dashi ya mayar dani kamar matarshi, gabaki daya na tare hotel dinda ya kama ina honey moon dina dashi mai makon mijina na sunna, sau dubu sai mun qare lalartamu deen yake kukan abinda ya aikata ni nake qarfafa mishi guiwa garin qarfafa guiwa ma sai na qara bashi kaina akoma ruwa nariqa na gama da rayuwar deen na Sangartashi da kaina, yanda baxai taba iya rayuwa da wata mace idan baniba.....
Tir da halinki naziah ��������...
Bacci mai dadi da nauyi cike da mafarkin deen dina..
ban farkaba sai guraren 11 na tashi na kimtsa mukayi break fast,
deen ya siyo min ticket daga abuja zuwa sokoto, shi kuma yace sai gobe zai dawo, bada son raina na rabu da deen dinaba amma ya xanyi dole in haqura,
na isa gida cike da murna da farin ciki bana tunanin komai sai deen dina, inna taji dadin yanda ta ganni nayi qiba tubarkalla dani, qirjjina ya cicciko Sosai, nima na kula da hakan, musamman lokacinda na zo abuja deen dina yake cewa na qara kyau da ni'ima qirjina ya cicciko dai dai hannunsa, na dauka santina yakeyi ashe da gaskene, munsha hira da inna Sosai,
sai guraren maqreeb yaya ya dawo muka gaisa dashi yaji dadin ganin yanda nayi kyau, autan inna waje ta karbeki, na kyalkyale da dariya, ai yaya waje ta hadune naijarmu ce sai a hankali..!! munyi hira sosai dasu, anan nakejin yaya wai zai auri Zainab khalifa, abin mamaki yarinyar da ya tsana kuma ya raina wai itace har yake ce mata honey a waya,Lallai soyayyah soyayyah ce,
sai guraren 10 na dare sannan na koma gidana duk na gaji ga kaya niqi niqi dana niqo..
ina zuwa sai bacci ya kwasheni, ban farkaba sai kusan asuba, nayi sallah nashiga aikin gida ko ina na gyara duk yayi qura na aikatu amma kuma gidan sosai yayi kyau gidan na chanxa mai fasali..
guraren la'asar sms yashigo" GOBE KISHIRYA KIYI GIRKI SU YAYA XASUZO SU MIKI SANNU DA DAWOWA"
mtwss shi wannan mutumin shirmensa yayi yawa..
Na Shirya musu girki kala kala,
Cikin kayan da deen dina ya siyo min na fitar musu da tsaraba, sunxo sunji dadin ganina da sukayi na kula da matar yayan nura sai kallona take tana murmushi motsi kadan tace mini sannu, araina nace matar nan tana sona, naji dadin zuwan su, sun tafi sun barni da Kewa...
Na isa Turkey...
Ai nasan kin isa Turkey Ya karanta sms din yayi dariyar mugunta nura kenan...
A Turkish naji dadin qasar duk da cewa ita ma akwai tsadar rayuwa amma tafi Cyprus arha..
sai da na shalle sati biyu anan, nayi kewar deen fiye da ko wane lokaci,kullum muna waya muna faranta ran juna, danma kar ya ga jarabata tayi yawa ya rainani da tuni nace ya biyoni Turkey,
amma dole in kama kai, ko yanzu dai na more, "wawiya"
Haka na qare zama Turkey na wuce India ba nura ba labarin sa nayi xaton xamu hadu koda sau daya ne amma ina...
a indiya nayi wata daya cur dan qasar tafi su dadi da kuma sauqin rayuwa, duk kudina da suka rage a India na qarar dasu...
a India ne na fara wani zazzabi zazzabi, amma dai ban baiwa zazzabin hadin kai ba dan kada ya rage min jin dadina, har yaren India na koya dan xaman da nayi, na hada tsarabata da wacce deen ya siya mun da wacce na siya na biya kudin kilo na dawo gida, a abuja na sauka, nayi waya gida na gaya musu na iso gida, ina mijin naki nayi dumm,ko baya kusa idan yaxo ki gaidashi, nace aah ai sai qarshen sati zai Dawo....
, sukace to Allah ya dawo dashi lafiya nayi waya da deen dina na gaya mishi ina abuja yace in kama hotel in jirashi yazo, haka kuwa akayi na kama hotel, shima gobe ya iso, aranar kwana mukayi muna abu daya, deen ya nuna min yanda yayi missing dina nima na nuna mar munji dadin juna.....Tir daku.��
Har deen yake cewa Asia ta karbeki kalli yanda qirjinki ya cicciko, na rufe fuskata na fada qirjinsa, yayi murmushi yana shafani a hankali, tabbas da ba deen ban san yanda rayuwata zata kasanceba, banajin ko za'amutu zan baiwa nura kaina a matsayin mata, haka bacci ya daukeni bacci mai dadi da nauyi inata mafarkin deen dina....
A mota matar yayan nuru take ma yayan nuru gulma wai inada ciki,
Kaga yaronnan mutumin banxa yana nuna ma mutane bai damu da naziah ba Ashe munafukin yana xagawa kaganta har da ciki, murna a gurin abban Fatima kamar me, kamar ma ba'ataba musu haihuwa ba, a hirar har an saka suna yaran da naziah xata haifa,
idan macene sunan mamar nura idan kuma namijine sunan marigayi baban naziah, kunji mutane da iyayi.....
Dan aikin da nayi na gaji Sosai na kwanta sai bacci, na tashi da wani irin xaxxabi da kasala na kula aikin da nayine ya haifar min dasu tunda da muna gun honey moon bana komai deen dina yake mun, a India ma nayi irin wannan xaxxabin Nasha panadol naji sauqi....
Nura ma ya dawo Sokoto munanan kamar yanda muke ba wani bayani har yau nakai wata uku da Kwana ashirin jikina ya bude, nayi qiba na gara kyau dani sai missing din deen dina nakeyi...
Na dauko waya na kira deen muna hira nake gayamai fa lokaci yayi ya kitsa min abinda xan fada ma mijina ya sakeni nima yace min akwai wani abu da yake jira yana kammala shi xai sallami matar tashi kamin lokacin na kammala idda na sai muyi aure....
Suna kammala waya jikinta na rawa ta dauko dayar wayan da nura ya bani dama dashi take mai SMS. Bata taba kiran saba Shima bai taba kirantaba,
Duk abinda deen dinta ya fada taga idan ta fadamai xai rainata my be ma yaqi sakinta sai kawai ta chanxa shawara ta tsara yanda xata mai haka kuwa akayi ta aika SMS tana jiran reply....
Abin mamaki ba musu ya aminta da buqatar ta na ya saketa amma da sharadin cewa sai nihal ta dawo ta ganta sannan xata tafi gidan su amma yanxu xai bata takarda tayi ran tsawa akan ta yarda.....
Itama ta amince da sharadin sa duk a SMS suke maganar,
Nan take nura ya rubuta takardar saki ya ijiye ma naziah a hanyar dakinta,
murna kamar ta kasheta yau xata kai ga burinta,ya deen dinta xaiji idan yaji ta karbo takardar saki,murna ba'a magana,
kamar ta wuce gida amma sai tace bari dai ta cika alqawari kuma taga wannan nihal da akeji da ita,kowa xancenta yakeyi xata dawo karatu canada, kuma tace gidansu xata sauka...
Naziah na Kwance tana yan tunane tunanenta, yanda aurenta da deen xai Kasan ce tunda yanxu ta xama baxawara, a bikin Su tayi kaxa tayi kaxa, a wannan tunanin ta gangaro wani tunani..
Sai yau nake tuna cewa fa...
tunda nayi aure banyi al'adaba ko sau dayaba..
Sai yau nake tuna dan ciwon dane da yawan xaxxabin da nakeyi..
Yanxu nake fahimtar inajin cikin cikina kamar ana min motsi..
Sai yau na tuna duk kwanciyar da nake da deen dina a jikina yake xube min.....din bai taba amfani da condom ba!!!
Lokaci daya hankalina ya tashi lallai ni lafiyayyace kuma komai xai iya faruwa dani,
Kardai ciki nake dashi???
Wai ma idan nayi ciki ya xan kalli inna, gashi na kashe aurena rana ta farko da naziah ta fara nadamar abinda ta aikata gashi ta karbi takardar rabuwa da nuraya xatayi???
Ta Shiga kogin tunani Lallai mafita itace taje asibiti Dr ya dubata, ba shiri tadauki key Sai wani prvt hospital, ta fara yima Dr bayani abinda ya kawota,
Bayan bincike bincike Dr ya gane cikine da ita Dr yaxo yana fada, ke kinsan kinada ciki amma bakixo aka dubaki ba sai yau, to lallai jaririnki yan......
Batamaji abinda Dr yace ba ta fadi sumammiya....
likitoci sukayo kaina aka samu ta farfado ta fara sun batu,
Dr dan Allah kataimakeni Dr ka rufamin asiri ya xanyi da rayuwata...!! shi Dr yadauka taji abinda ya fada ne na cewa yaron cikinta na cikin matsala kuma cikin xa iya xubewa ko wane lokaci.. hakan yasa yake bata haquri da magana tare da alqawarin kasan cewa Dr ta har ta Sami sauqi, ya rubuta maganguna da allurai da kuma abincin da xata riqaci...
Ta dawo gida cike da xullumi,da tunani, shin xata fara fadama deen labarin cikin da take dashi ne?? ko kuma ta fara da maganar sakin da aka matane,?? "Nima dai jabo sai kallonta nakeyi" tadai yanke shawaran Sanar dashi xancen cikin b4 sakin....
dama bata tafi phone dinta ba,
Ta kira deen dinta, koda taxo ya kira har 8,ta kira
He'll hulwatiy ya kike ina kika shiga inata kira baki dauka ba.??
Hello ko baki jinane?? har xai kashe sai yaji maganarta a hankali,
Inajinka deen!!!
Lafiyan ki kuwa??
Naje hospital ne...!!
Subhanallahi hulwatiy mi yake damunki??
Waye bashi da lafiya??
Kimin bayani mana kinyi shiru...
Na fara magaba ka katseni shi yasa nayi shiru..!!
Sorry hulwatiy kinsan Banason abinda xai taba min lafiyar kine ko kadan, kece jina kece ganina.. kece duk wani buri na rayuwata...!!!
Talk to me please m hulwatiy.!!
Tayi ajiyar numfashi,
Daxu Dr y dubani...
Eh inajinki ci gaba, miyake damunki mi Dr yace??
Yace wai inada juna biyu...
What..!!????
Eh yace ciki nake dashi, haba hulwatiy,
Kidaina min irin wannan wasan mana!!
Kamar ya Wasa
Wallahi deen da gaske nakeyi.
Hankalin deen ya tashi matuqa, ya Rasa abin cewa,
Ok ki bari anjima xan kiraki yanxu inajin maganar wannan shasha shar tana zuwa kada taji mi muke fada!!
Amma ai yau Monday deen daxu kace min kana office ne!!!
Eh ina office inaga tanada buqatar kudine taxo gurina!!
Amma kace min baka taba ganinta ba ya akayi har kake gane muryarta.??
Anya deen!!!!
No kingane ai......
Sai taji sallamar mace a wayar kuma taji an kashe aranta tace ee naji muryar mace inaga ta biyo shine, sai bata gane komai, kuma bata taba tunanin yaudara a gurin deen ba.
Da farko kuma har taji tsoro,
Amma fa ita dole deen yaxo a xubar da cikin nan kamin tayi yun qurin barin gidan aurenta, aranta ta riqa saqe saqe har bacci ya dauketa
A bangareen deen kuwa yanata saqe aran shi yanda xa'ayi da ckin nan, shikam bai San yanda xaiyi da itaba, kuma yasan illar xubar da ciki dan xata iya mutuwa, kuma dole Shi xaikaita hospital kuma shi xaiyi sign Lallai baxai iyaba...!! idan ta mutufa??
Miye mafita??
Mafita dayace kawai ka rabu da matar mutane kaje ka rungumi matarka!!!
Idan nayi haka anya na mata adalci???
Lallai nayi kuskure nayi jahilci tarayya da matar aure,
Haka ya qare tunanensa qarke ya yanke cewa xai rabu da ita kawai taSan yanda xatayi da cikin......
Kinji mugu dan iska kadan daga cikin halayen sheguuuu..��
bata farka ba sai guraren maqreeb, tasan ma deen ya kira, a gurguje tayi sallah bata qareba aka kira maqreeb tayi maqreeb tayi addu'a ta janyo waya..
Ta duba wayam ba miss call ko daya abin ya bata mamaki matuqa. Ta daure ta kira shi sai na uku ya dauka,
Hello deen...
Hello deen,
Hello...Kanajina kuwa?
Eh inajinki.!!
Ya naji kana magana fada fada.??
Waya tabamun kaine??
Kedai ki fadi abin da xaki fada kawai.!!
Tayi shock dajin wannan maganar a bakin deen, wanda daidai da rana daya bai taba mata koda gaddama ba bare ya mata baqar magana.!!
Tayi ajiyar xuciya,
Allah ya baka haquri, dama maganar cikinnan ne nace ya xa'ayi dashi.??
Kuma dama inason in gayamaka na karbi takarda sakina..!!
Deen yayi duuum jin wannan maganar ta hulwaty, Lallai maisha ta riqa tasha ba abinda yafi illa ya fatattaketa ta rabu dashi, amma ya mata adalci kuwa? Anya yiyiwa kanShi da son da yake mata adalci kuwa?
Anya xai ma iya rayuwa ba hulwar sa, xaka iya mana dayan xuciyar ta bashi amsa....
Takeshi daga dogon tunanin da ya tafi, deen kayi shiru deen!! ,
Yanda ta fadi maganar da murya mai Sanyi sai ta qara bashi tausayi.!!
No Inajinki ci gaba..
Ai na fadi duk abinda xan fada.! Kai nake jira...
Dama ke duk abinda mukeyi dake kinSan bakiyi planing ba??
Dan ki xubar min da mutunci yasa kikayi tarayya dani?
Akan me xaki bari ciki ya Shiga,??
Ta yaya xan aureki da ciki??
Sam bakiyi tunaniba kuma bakiyi naxariba, ni Muslimine baxan taba yin shirka gurin xubar da cikiba, Sabida haka kisan yanda xakiya da cikin ki, ki nemi mijinki kuyi Sulhu ya rufa miki asiri ba hannuna ac......
Deen kaine kuwa..!!? Ta Katse shi cike da mamakin abinda yake fitowa daga bakin deen mi yake Shirin faruwa da itane abin kamar a mafarki...
Ki saurareni ya fada yana mai daqa murya.!!
Daga yau Sai yau kada ki qara nemana..!! kadama ki qara nuna kinSanni.!! jahilar banxa wacce batada tunanin..
Namiji rigar qaya inji mata kadan daga cikin aikin maxa kenan dan haka mata akiyaye..!